Sunday 26 May 2019

Taron Buda bake na Kungiyar Hausawan sudan ta kasa da kasa ofishin Sinnar karamar hukumar Umshoka

Da sunan Allah mai rahama mai jikai
kungiyar hausawan Sudan ta ƙasa da ƙasa
reshen sudan ofishin jahar( sinnar) karamar hukumar (amshoka)
 ranar 19 ga watan azimi wanda yayi daidai da ranar 24/05/2019 tayi gaga rimin taron buɗa baki a jahar ta sinnar wanda ya sami halar tar mutane da dama sosai daga ƴan garin bayan anyi buɗa bakin sai aka soma tattaunawa inda ɗan uwan mu wato ( umar abubakar ) wanda shi ma aikacine a ma'aikatar labarai ta ofishin jahar sai malan (abdul'aziz abdullah)wanda yana cikin wanda suka tsaya sosai wajen ganin an ƙaddamar da makarantar alya'fien ) sannan sai maganar malan (hamza yusuf ) wanda shine yazo amatsayin wakilin (dindir) sai mai wakiltar (faƙad ) wato ali muhammad ) sannan sai maganar mai wakiltar kungiyar (amshoka) malan anas mustafa) yakasance anrife taron da maganar shugaban ofishoshi na jahar wato malan (babikir ali umar ) wanda ya soma da godewa wanda su suka soma wannan farar tafiya mai farin aiki da zummar allah ya saka musu da alkairi amen kamar irin su dakta ( hasan waƙi allah) da ( dakta ahamed ali ) muna tawasali da wannan aiki da sukai allah yasa saka musu da mafificin alkairi amen sannan yai bayani akan wannan ƙungiya akan aiyukan ta da takeyi musammam yadda tame da hankali akan karantar wa da tarbiyantar da yara wanda sune manyan gobe sannan ya fadakar akan matasan wannan ƙabila da su kula sannan su guji duk wani tashin hankali da zai shafemu da kuma ƙabilar mu baki ɗaya sannan ya tsananta akan kungiya da aikinta da ta kula da duk wata ɓaraka da ta tasowa wannan ƙabila baki ɗaya sai magana ta shida wacce shugaban kungiyar na amshoka yayi bayan haka sai taron ya ƙare wanda hakan ya ƙara sa jituwa tsakanin matasan ) amshoka) da na dindir) da na faƙad) da na murafa) kamar yadda kungiyar ta ke miƙa godiyar ta ga wayenda suka temaka da lokacinsu da karfinsu da kuɗinsu sanarwa daga ofishin jahar



No comments:

Post a Comment